19/01/2025
Hajjin bana: IHR ta yaba wa NAHCON bisa canja kamfanin hidimar alhazai a Saudiyya
Kungiya mai zaman kan ta da ke kawo rahotanni kan Hajji da Umrah, IHR, ya yabawa hukumar alhazai ta kasa NAHCON bisa zabar sabon kamfanin hidimar alhazai a Saudi Arebiya domin gudanar da aikin hajjin 2025.
IHR ta ce matakin zai haifar da gasa mai kyau a tsakanin kamfanonin yi wa alhazai hidima da su rika yin aiyuka masu inganci ga mahajjatan Najeriya.
IHR a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun kodinetan ts na ƙasa, Malam Ibrahim Muhammed a birnin Makkah na kasar Saudiyya, ta ce neman inganta aikin Hajji ya kasance babban kalubale ga alhazan Najeriya sakamakon gazawar da aka yi na samar da gamsassun ayyuka.
Saboda haka kungiyar ta yabawa NAHCON boss wannan mataki, inda ta ce zai samar da ingattun hidimomi ga alhazan Nijeriya a Saudiya yayin aikin Hajji.
16/01/2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnoni sun ƙi amince wa da ƙarin VAT
Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta yi watsi da matakin kara harajin kayaiyakin masarufi (VAT).
A ƙarshen wata ganawa a Abuja a yau Alhamis, gwamnonin sun ce matakin bai dace ba.
Gwamnonin sun kuma bayyana goyon bayansu ga yadda ake gudanar da ayyukan majalisa na kudurorin dokar haraji.
A shekarar da ta gabata ne dai, shugaban kwamitin shugaban kasa kan manufofin kasafin kudi da sake fasalin haraji, Taiwo Oyedele, ya ce kwamitin ya gabatar da wata doka ga majalisar dokoki ta kasa don kara harajin VAT daga kashi 7.5% zuwa kashi 10% na yanzu.
Sai dai kuma gwamnonin sun amince da cewa bai kamata a kara harajin VAT ko rage harajin Kamfanoni ba (CIT) a wannan lokaci, don tabbatar da daidaiton tattalin arziki.
Taron ya ba da shawarar ci gaba da keɓance kayan masarufi da kayan amfanin gona daga harajin VAT don kiyaye walwalar 'yan ƙasa da haɓaka aikin noma.
07/12/2024
Ko kun san Mene ne wannan?
28/10/2024
Yadda mataimakin shugaban Nijeriya ke yi wa Shugaba Tinubu bayanin abubuwan da s**a faru a Nijeriya lokacin da Tinubun ya tafi hutu. Fadar shugaban kasar ta ce ganawar ta shugabannin biyu ta wannan Litinin ta bai wa Kashim Shettima damar yi wa Tinubu bayanin muhimman abubuwan da s**a faru a taron kasar Sweden da Tinubu ya tura shi don ya wakilce shi