03/03/2025
Muna Neman A Yiwa Comrd Shamsu Adalci Wanda DSS S**a K**a - Inji Yan'uwansa
Yan'uwan shugaban Matasan jihar Katsina (Chairman National Youth's Council of Nigeria, Katsina Chapter) Comr. Shamsu Ibrahim sun nemi a yiwa ɗan'uwansu Adalci, wanda jami'an tsaron farin kaya DSS s**a k**a har tsawon kwanaki 26, ba tare da wani kwakwaran laifi ba.
Yan'uwan sun tabbatar da cewa an kai shi kotu daga can aka wuce da shi gidan yari ne ba tare da an bada shi bailing ba, bisa zargin tayar da hankali a cikin jama'a.
Saidai yan'uwan sun musunta cewa ba gaskiya ba ne, mutum ne da ke zaune da kowa lafiya, don haka suke neman hukumomin tsaro da Gwamnan jihar Katsina mai girma Dr. Dikko Umaru Radda da su sanya baki cikin lamarin, domin ganin an yi masa Adalci.

02/02/2024
17/01/2024
11/01/2024
07/01/2024
11/12/2023
18/06/2023